|
Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon ya yi duba ne kan yadda hukumar kulada kwallon kafar Afrika CAF ta fitar da jerin alkalan wasan 85 da zasu yi alkalanci a gasar lashe kofin nahiyar da za a yi a Cote d’Ivoire a shekara mai zuwa, sai dai abinda ya fi daukar hankali a ciki shine yadda ba a hango koda sunan alkalin wasa daga ba daga Najeriya wacece ake ganinta a sahun gaba-gaba wajen sha’anin kwallon kafa a nahiyar. Wannan dai bashi ne karo na farko da kasar ke fuskantar irin wannan matsalar ba, domin a ida aka waiwaya baya a gasar da aka gudanar a kasar Kamaru a shekarar da ta gabata, alkalin wasa daya ne rak ya wakilci Najeriya shima a matsayin mataimakin alkalin wasa. Ku latsa alamar sauti domin sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh..... |