|
Shirin 'Duniyar Wasanni' a wannan mako ya mai da hankali ne kan batun nasarar dawowa gasar Firimiyar Najeriya da kungiyoyin Kano Pillars da Katsina United suka samu a karshen makon jiya. Kamar yadda aka sani ne dai dukkanin kungiyoyin biyu wato Kano Pillars da Katsina United sun rikito zuwa aji na biyu ne a gasar ta Firimiyar da ta gabata, bayan gaza tabuka abun azo agani, abunda yasa suka karkare a ajin ‘yan dagaji. To sai dai kuma cikin wani abun mamaki dukkanin su sunyi kukan kura sun koma gasar bayan kwazon da sukayi a gasar aji na biyu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh... |