|
Description:
|
|
Yanzu haka ana ta kokarin samar wa arewacin Nijeriya sabuwar makoma. Wannan na zuwa ne sakamakon yadda yankin ke komawa na baya ga dangi.
Ababen da yankin ke tinakaho da su a baya, da suka hada da dawwamammen zaman lafiya, tsaro, albarkar gona, ingantaccen ilimi, adalci da girmama na gaba, sun zama tarihi.
Maimakon wadancan, yanzu ba abin da ke addabar sassa daban-daban na yankin sune tashe-tashen hankula, kashe-kashen kabilanci da na addini, matsalar ilimi, talauci da watsi da aikin gona da suka mamaye yankin.
Shirin DUNIYAR MU A YAU, na wannan makon, ya duba wannan batun, kuma Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masu ruwa da tsaki daga yanki na arewacin Nijeriya.
Shirin ya kuma leka fagen siyasar kasar ta Nijeriya, inda ya duba muhimman batutuwa a yankin na arewa.
... a yi saurare lafiaya. |